Wane ne ke so a cire tallafin man fetur a Najeriya?

Wane ne ke so a cire tallafin man fetur a Najeriya?


Buhari

ASALIN HOTON,STATE HOUSE

Tsawon shekaru da dama, gwamnatoci a Najeriya na cewa suna so talakawansu su sayi man fetur a farashi mai sauƙi ta hanyar ware kuɗi domin ba da tallafi.

Sai dai wasu alƙaluma da gwamnati ke fitarwa sun nuna cewa ana kashe kusan naira biliyan 250 duk wata a matsayin kuɗin tallafi, wanda gwamnati a yanzu ke cewa ya yi yawa kuma tana so ta yi amfani da su a wasu ayyukan raya ƙasa.

Batun cire tallafin ya mamaye kanun labarai a Najeriya a wannan makon, kuma mutane suna ta tsokaci a shafukan sada zumunta.

Duk da cewa wasu gwamnatoci a baya ba su yi nasarar ba a yunƙurinsu na cire tallafin, gwamnatin Shugaba Buhari ta ci alwashin cire shi biyo bayan kafa sabuwar dokar man fetur ta Petroleum Industry Act (PIA), wadda ta mayar da kamfanin na kasuwanci zalla maimakon na gwamnati ita kaɗai.

Sai dai kuma bayanai masu cin karo da juna sun fara ɓulla daga fadar gwamnatin a baya-bayan nan kan cirewa ko barin tallafin, wanda farashinsa zai kai kusan N300 idan gwamnati ta yi nasarar cire shi.

Yayin da Ministar Kuɗi ke cewa an saka ƙudirin a cikin kasafin kuɗi na 2022, shi kuma Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan na cewa Shugaba Buhari ya faɗa masa cewa bai umarci kowa ba ya cire tallafin.



Nan da wata shida za mu daina biyan tallafi - Ministar Kuɗi Zainab Ahmed

ASALIN HOTON,FACEBOOK/ZAINAB SHAMSUNA AHMED

Bayanan hoto,

Minista Zainab Shamsuna ta ce daga wata shida na farkon 2022 za su daina biyan tallafin fetur

A watan Oktoban 2021, Ministar Kuɗi Zainab Shamsuna Ahmed ta bayyana wa 'yan ƙasa cewa gwamnati ta shirya domin mayar da harkar man fetur ta 'yan kasuwa zalla, tana mai cewa kuɗin da za a biya tallafi na wata shida na farkon 2022 kawai suka saka a kasafin kuɗi.

Comments